Jam'iyyar Dimokuradiyya ta Najeriya, NDC, ta ware tikitin takarar shugaban kasa na 2027, na tsawon shekaru hudu, zuwa kudancin Najeriya.
Shawarar ta biyo bayan amincewa da kudirin da Afam Victor Ogene, dan majalisa mai wakiltar mazabar Ogbaru ta jihar Anambra a majalisar wakilai ya gabatar a taron kasa na jam'iyyar.
Wakilan taron sun amince da kudirin
Bugu da kari, an yanke shawarar cewa bayan kammala wa'adin shekaru hudu, za a bai wa Arewa tikitin takarar shugaban kasa ta atomatik.
Kudurin ya share hanya ga Peter Obi, tsohon gwamnan jihar Anambra, tare da sauran 'yan takarar kudu, don siyan fom din takarar shugaban kasa na jam'iyyar kafin zaben fidda gwani.
Obi da tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Kwankwaso, kwanan nan suka sauya sheka zuwa NDC.
Ana sa ran cewa 'yan takarar biyu za su daga tutar jam'iyyar a zaben shugaban kasa a 2027.
